12 Agusta 2024 - 10:30
Falasdinawa 12 Ne Suka Yi Shahada A Harin Da Yahudawan Sahyuniya Suka Kai A Khan Yunis

Majiyoyin labarai sun ba da rahoton ci gaba da kai hare-hare da gwamnatin sahyoniyawan ke kai wa zirin Gaza da kuma shahadantar da Palastinawa 12 a lokacin da sojojin wannan gwamnati suka kai harin a "Khan Yunis" da ke kudancin wannan waje.

Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na Ahlul-Bait (a.s) ya habarta maku cewa: sojojin yahudawan sahyoniya suna ci gaba da yin kisan kiyashi a zirin Gaza a yau din da ake cika rana ta 311 a jere ta hanyar kai hare-hare ta sama da harsasai da kashe fararen hula a cikin wani mummunan yanayi na jin kai sakamakon hare-hare da sojojin suke ci gaba da kaiwa Mazauna wannan yanki wanda  su kaiwa kawanya.

Dangane da haka ne tashar Al-Mayadeen ta bayar da rahoton cewa, jirage marasa matuki na kunar bakin wake na gwamnatin sahyoniyawan sun yi ruwan bama-bamai a wani gida da ke unguwar "Absan Al-Jadedeh" da ke gabashin Khan Yunus.

Wakilin Al-Mayadeen a zirin Gaza ya sanar da cewa: An mika shahidai 12 zuwa asibitin "Nasser" sakamakon harin bam da yahudawan suka kai a Khan Yunus.

A cewar wani rahoton, Falasdinawa 2 ne kuma suka yi shahada sakamakon harin bam da aka kai a kofar shiga sansanin Al-Nusirat da ke tsakiyar zirin Gaza.

Sannan a ci gaba da aikata laifukan na yau jiragen yakin Isra'ila sun yi ruwan bama-bamai a wani gida da ke unguwar Al-Sheikh Rizwan da ke arewacin zirin Gaza.